1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Burkina Faso ta sake dakatar da wasu kafafen yada labarai

Abdulkarim Muhammad Abdulkarim
April 29, 2024

Dakatarwar ta yanzu ta shafi Deutsche Welle da ke nan Jamus, da jaridar Faransa ta Le Monde, da Quest-France, sai jaridar Guardian ta Burtaniya da kamfanonin dillancin Afirka na APA da kuma Ecofin

https://p.dw.com/p/4fHZS
Hoto: Issouf Sanogo/AFP

Burkina Faso ta sake dakatar da wasu kafafen yada labarai daga yada shirye-shiryensu a kasar, sakamakon fitar da rahoton hukumar kare hakkin bil'adama ta Human Rights Watch, da ta zargi sojojin kasar da yi wa wasu mutanen karkara fararen hula 223 kisan gilla.

Karin bayani:Burkina Faso ta yi fatali da zarge-zargen Human Rights Watch

Kafafen yada labaran da dakatarwar ta yanzu ta shafa sun hada da Deutsche Welle da ke nan Jamus, da jaridar Faransa ta Le Monde, da Quest-France, sai jaridar Guardian ta Burtaniya da kamfanonin dillancin Afirka na APA da kuma Ecofin.

Karin bayani:Burkina Faso ta dakatar da shirye-shiryen BBC da VOA

Tun da farko dai Burkina ta fara dakatar da BBC da VOA, da kuma gidan talabijin din Faransa na TV5Monde.

Karin bayani:Ana zargin sojojin Burkina Faso da kashe fararen hula 223

Rahoton na Human Rights Watch ya zargi sojojin Burkina Faso da hallaka fafaren hular 223 a cikin watan Fabarairun da ya gabata, bisa zarginsu da hada baki da 'yan ta'adda.